Allah shi ne mai gaskatawa mai mamaye dukkan komai

Allah shi ne mai gaskatawa mai mamaye dukkan komai

Allah shi ne mai gaskatawa mai mamaye dukkan komai

Shi ne Allah mai gasgatawa mai kulawa.. “Shi ne Allah wanda babu abin bautawa da gaskiya sai shi, mai mulki, tsakakakke, mai aminci, mai gaskatawa mai kulawa” (Al-hashru : 23)

“Mai gaskatawa” .. Wanda ya yabi kansa da siffofi na kamala, da kamalar cika da girma, wanda ya aiko manzanni ya saukar da littattafai da ayoyi da hujjoji, ya gaskata manzanninsa da kowace aya da hujja, wadda take nuna gaskiyarsu da ingancin abin da suka zo da shi.

“Mai amintarwa”

Wanda ta hanyar wahayinsa yake yaxa aminci a tsakanin bayinsa, da zaman lafiya a tsakanin halittarsa, da nutsuwa. “ya amintar da su daga tsoro” (Quraish : 4)

“Mai amintarwa”

Amintacce, wanda ya mamaye dukkan komai, mai shaida akan bayinsa da abin da suke yi.

“Amintacce”

“Mai kulawa”.. Mai ganin voyayyun al’amura da abin zukata suka voye, wanda ya kewaye komai da ilimi.

Wanda ba ya rage lada, ba ya qara uquba. Shi ne mafi cancantar wanda ya yi qari, da ya kyautata.

“Mai kulawa”

Ya mamaye bayinsa, ya rinjaye su, ya kula da su, yana ganin ayyukansu da halinsu, yana kewaye da su, duk wani abu mai sauqi ne a wajensa, kuma komai yana da buqata a wajensa. “babu wanda ya yi kama da shi, shi mai ji ne kuma mai gani” (Asshura : 11)

Shi ne Allah mai gaskatawa mai kulawa



Tags: