Allah mai tausasawa ne

Allah mai tausasawa ne

Allah mai tausasawa ne

Shi ne Allah mai tausasawa.. “Haqiqa Ubangijina mai tausasawa ne ga wanda ya ga dama” (Yusuf : 100)

Mai tausasawa

Wanda yake horewa halitta wata halittar don tausasawa da jin qai da qauna.

Mai tausasawa

Mai bayar da manya – manyan kyaututtuka masu yawa,

“Mai tausasawa”.. Wanda iliminsa ya kewaye dukkan abin da yake voye da fili, ya san voyayyu da qananan abubuwa, mai tausasawa bayinsa muminai, mai sada su da maslaharsu da tausayinsa da kyautatawarsa ta hanyar da ba su sani ba.

Mai Tausasawa

Mai tausasawa bayinsa.. “Allah mai tausasawa bayinsa ne” (Asshuura : 19)

Yana ba su abin da yake alheri a cikin addininsu da duniyarsu, ya kuma kare su daga abin da yake sharri gare su a duniyarsu da addininsu.

Mai tausasawa

Gannai ba sa iya riskarsa, shi ne yake riskar gannai… “Gannai basa iya riskarsa, shi ne yake iya riskar gannai, shi mai tausasawa masani mai ba da labari” (Al-an’am : 103)

“Mai tausasawa”

Ya san voyayyun abubuwa, yana lissafa qananan ayyuka, babu wani abu da zai vuya gare shi da dare ko rana. Ya san abin da ya dace da bayinsa, qanana da manya, yana tausaya musu.

Mai tausasawa

Yana tausasawa bayinsa idan ya hukunta wani lamari, yana taimaka musu idan ya qaddara abu, yana buxe musu qofofin farin ciki idan lamarin ya tsananta, ya kawo musu sauki idan lamari ya ta’azzara.

Lallai Shi ne Allah mai tausasawa



Tags: