Allah wanda ake nufa da buqata

Allah wanda ake nufa da buqata

Allah wanda ake nufa da buqata

Haqiqa Allah shi ne wanda ake nufa da buqata.. “ka ce shi ne Allah xaya. Allah wanda ake nufata da buqata” (Al-ikhlas : 1 – 2)

“Wanda ake nufa da buqata”

Cikakke a sunayensa da siffofinsa, ba wata tawaya ko gazawa dake samunsa

“Wanda ake nufa da buqata”.. Wanda halittu gabaxayansu suke nufa da dukkan buqatunsu da lalurorinsu da halayensu, saboda kamalar cikarsa, a zatinsa da sunayensa da siffofinsa da ayyukansa.

“Wanda ake nufa da buqata”

Mawadacin da kowa yake buqatarsa, shi kuma ba ya buqatar kowa.. “yana ciyarwa shi kuma ba a ciyar da shi” (Al-an’am : 14)

“Wanda ake nufa da buqata”

Ubangiji mai jujjuya al’amura, mai mulki, mai tasrifi.

“Wanda ake nufa da buqata”

Zukata sun fuskance shi da buqatu, ya ba su bai hana su ba, sun kirawo shi akan buqatunsu, ya yaye musu damuwa ya amsa musu. Waxanda suka bar shi sun kirawo shi ya ba su, waxanda suke jin tsoro sun koma wajensa ya amintar da su, masu tauhidi sun yi fata a wajensa, ya ba su abin da suka yi fata, waxanda suke cikin musiba sun kirawo shi, ya kuvutar da su, dukkan bayi sun sunkuyar da kai gare shi.

Haqiqa shi ne Allah wanda ake nufa da buqata



Tags: