Yana daga cikin fa'idojin imani abin da zai zo

Yana daga cikin fa'idojin imani abin da zai zo

Daga Fa’idojin Ikhlasi

1-Karvar ayyuka : Wanda wannan abu ne mai mahimmanci, kuma sharaxi ne daga sharuxxan karvar ayyuka. Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Haqiqa Allah ba ya karvar aiki sai wanda ya kasance an yi shi da tsarkakakkiyar zuciya, kuma an yi don neman yardarsa” (Nasa’i ne ya rawaito shi)

2-Samun Nasara da kafuwa : Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Allah yana taimakon wannan al’umma da raunananta, ta hanyar addu’arsu da sallarsu da Ikhlasi” (Nasa’i ne ya rawaito shi)

3-Kuvutar zuciya daga cututtuka : Ina nufin cututtukan zuciya, kamar qullata, da qyashi, da ha’inci, da hassada. Manzon Allah (S.A.W) ya faxa a lokacin hajjin ban kwana ya ce, “Abubuwa guda uku zuciyar musulmi ba ta qullata a kansu : Tsarkake aiki ga Allah, yi wa shugabannin musulmi nasiha, lizimtar jama’ar musulmi. Domin addu’a tana kewaye da su” (Tirmizi ne ya rawaito shi)

Abdullahi xan Umar ya ce, &"Da na san Allah ya karvi sujjadata guda xaya, da sadakar dirhami xaya, da babu abin da zan fi so kamar mutuwa. Kun san aikin wa ake karva? &"kaxai Allah yana karva daga masu tsoronsa ne&"

4-Haxa ayyukan duniya da ayyuka na qwarai : Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “A cikin tarawar xayanku da iyalinsa akwai ladan sadaka. Sai suka ce, ya Manzon Allah, yanzu xayanmu zai biya sha’awarsa kuma ya zama yana da lada? Sai Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Ku ba ni labari idan ya sanyata a haramun yana da alhaki? To haka ma idan ya sanyata a halal, to yana da lada” (Muslim ne ya rawaito shi)

5-Korar munanan saqe-saqen Shaixan da wasiwasinsa : Yayin da Allah ya kori Shaixan ya nisantar da shi daga rahamarsa sai Allah ya faxa mana abin da ya ce, ”Ya ce, ya Ubangijina saboda vatar da ni da ka yi, sai na qawata musu (Varna) a bayan qasa gabaxayansu. Sai dai bayinka cikinsu waxanda aka tsarkake” (Alhijri : 39 – 40)

Ta yi wu wani ya nisanci duniya da jikinsa, amma kuma yana tare da ita a zuciyarsa. Ta yiwu wani kuma yana tare da duniya da jikinsa, amma kuma baya tare da ita da zuciyarsa, wannan shi ya fi hankali.

6-Yaye damuwa da wahalhalu : kamar misalin abin da ya kasance a cikin labarin mutanen nan guda uku, waxanda barci ko ruwan sama ya kora su zuwa ga wani kogo. Asalin hadisin yana cikin Bukhari da Muslim.

7-Tsira da aminta daga haxarin fitintunu : kamar yadda ya faru da Yusuf (S.A.W) Allah yana cewa a kansa : “Ta himmatu da shi, shi ma ya himmatu da ita, ba don ya ga dalilin Ubangijinsa ba, hakan ya faru ne don mu kawar masa da mummunan aiki da alfasha, haqiqa shi yana cikin bayinmu tsarkaka” (Yusuf : 24)

Ta yi wu aiki kaxan, niyya ta mayar da shi mai yawa. Ta yi wu kuma aiki mai yawa niyya ta mayar da shi kaxan.

Ibnul Mubarak

8-Samun lada koda kuwa aikin bai kai ba. Allah mai girma da buwaya ya ce, “Da waxanda idan sun zo wajenka don ka xauke su (zuwa jihadi) sai ka ce babu abin da zan xauke ku a kanshi, sai su juya idanuwansu suna zubar da hawaye don baqin cikin ba su samu abin da za su ciyar ba” (Attaubah : 92)

Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Duk wanda ya roqi Allah shahada da gaskiya, to Allah zai kai shi matsayin Shahidai, koda kuwa ya mutu a kan shimfixarsa” (Muslim ne ya rawaito shi)

9-Shiga Aljannah : saboda faxin Allah Maxaukakin Sarki : “Ba komai ake saka muku ba, sai abin da kuka kasance kuna aikatawa”. (Assaafat : 39)

Ka voye kyawawan ayyukanka kamar yadda kake voye munanan ayyukanka.

Abu Haazim Al-madiniiy

Allah Maxaukakin Sarki ya ce, “Sai dai bayin Allah tsakakakku. Waxannan suna da wani arziki sananne. Kayan marmari kuma suna ababen girmamawa. A cikin aljannatai na ni’ima. Akan gadaje suna fuskantar juna. Ana kewayawa a cikinsu da kofi na giya ta wani marmaro. Fara sal mai daxi ga masu sha. Babu wani jiri a cikinta, kuma ba za su yi wani maye ba. Kuma suna da wasu mata masu taqaita kallonsu. Masu manyan idanu. Kamar su wani qwai ne voyayye” (Assaafat : 40 – 49)

Wannan yana cikin manya-manyan fa’idojin tsarkake zuciya



Tags: