Ta yaya za ka zama mai tsarkake zuciyarka?

Ta yaya za ka zama mai tsarkake zuciyarka?

Ta yaya za ka zama mai tsarkake zuciyarka?

Abu na farko : tabbatar da (Tauhidi) kaxaita Allah. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa, “Kana mai tsarkake addini gare shi. Ku saurara addini tsarkakakke na Allah ne” (Azzumar : 2 – 3)

Duk wanda baxininsa ya sava da zahirinsa, to wannan abu ne vatacce.

Allah Maxaukakin Sarki ya ce, “Ba a umarce su ba sai dai su bautawa Allah suna masu tsarkake addini gare shi” (Albayyinah : 5)

Na biyu : Tabbatar da biyayya ga Manzon Allah (S.A.W) da yi masa xa’a cikin abin da ya umarta, da nisantar abin da ya hana, ya tsawatar a kai, da gaskata shi cikin abin da ya ba da labari. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa,.. “Ya ku waxanda suka yi imani, ku bi Allah ku bi Manzosa, da ma’abota al’amura a cikinku, idan kun yi jayayya akan wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da Manzo, in har kun yi imani da Allah da ranar lahira, wannan shi ne mafi alheri kuma shi ne kyau ga fassara”. (Annisa’i : 59)

Na uku : Idan kana son ka samu Ikhlasi to ka yi qoqarin aiki na qwarai, ka riqa tunawa a koyaushe cewa daga cikin mutum bakwai da Allah zai musu inuwa ranar da babu inuwa sai inuwarsa, akwai : “Mutumin da ya yi sadaka ya voye ta yayin bayarwa”. (Bukhari ne ya rawaito shi)

Ka sake tunawa dai cewa : “Dukkan ayyuka sai da niyya” (Bukhari ne ya rawaito shi)

Na huxu : Ka watsar da son yabon mutane daga zuciyarka, ka xebe qauna daga abin da yake hannun mutane, ka mayar da komai naka zuwa ga Allah mai girma da buwaya. Mai tsarkake niyya mai yin abu don Allah baya kwaxayin wata duniya da zai samu, ko wata mace da zai aura, kwaxayinsa kullum shi ne rahamar Allah.

Na biyar : Ka koma ka faxi gaban Ubangijinka, ka lazimci bakin qofarsa mai girma da buwaya tare da yin addu’a Allah ya azurtaka da tsarkin zuciya, da barin riya, ya karvi tubanka daga abin da ya gabata na zunubai da savo.

Tsarkake niyya shi ne kada nemi wani ya san aikinka sai Allah, kada ka nemi wani sakamako daga wajen waninsa

Na shida : Nisantar riya da guje mata, Idan bawa ya shigar da kansa hanyar riya to ya qara nisa daga hanyar Allah. Misalin haka yadda wasu mutane suke kiran kawunansu da waliyyi, ko mutum ya yarda a kira shi da haka, ko ya riqa bayar da labarun ayyukansa da biyayyarsa ga Allah. Allah yana cewa, “Waxanda suke neman rayuwar duniya da adonta to za mu cika musu sakamakon ayyukansu a cikinta ba za a rage musu ba. Waxannan ba su da komai a lahira sai wuta, ayyukansu da suka yi sun rushe, abin da suke aikatawa ya lalace” (Hud : 15 – 16)

Riya qaramar shirka ce, amma rashin karvar aikin da ta shiga cikinsa koda kuwa a zahirinsa ingantacce ne, da mayar da shi ga waxanda suke yin shi, ya ishe ya nuna mummunar makomarta,

Na Bakwai : Zama da masu Ikhlasi. Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Mutum yana kan addinin abokinsa” (Tirmizi ne ya rawaito shi)

Ikhlasi da son yabon mutane bacsa haxuwa a zuciya, sai dai kamar yadda wuta da ruwa suke haxuwa.

Na takwas : Voye ibada da sirrinta ta. Allah Maxaukakin Sarki ya ce, “Idan kuka bayyana sadaka to madallah da ita. Idan kuka voyeta kuka baiwa mabuqata to wannan shi ya fi alheri gareku” (Albaqra : 271)

Na tara : Yiwa kai hisabi mai tsanani. Wato hisabi a koda yaushe. Allah maxaukakin Sarki ya ce, “Waxanda suka yi qoqari a kanmu za mu shiryar da su hanyoyinmu” (Al’ankabut : 69)

Ka lura da faxin Allah (S.W.T) “A kanmu”

Na goma : lizimtar addu’a, da fuskantar Ubangiji da yawaita hakan. Idan bawa faqiri ya lizimci qofar ubangidansa, sai ubangidan nasa ya tausaya masa, ya biya masa buqatarsa da abin da yake nema. Addu’a ita ce roqon Allah mai girma da buwaya.



Tags: