Ma'anar Tsakake zuciya

Ma'anar Tsakake zuciya

Ma&"anar Tsakake zuciya

Wanda duk ya san Allah sai ya so shi, ya tsarkake ibada gare shi

Ikhlasi shi ne aljannar masu Ikhlasi, kuma ruhin masu tsoron Allah, sannan shi ne sirri tsakanin bawa da Ubangijinsa, shi ne abin da yake yanke waswasi da riya. Ikhlasi shi ne ka yi nufin Allah da aikinka, kada ka nufi waninsa, kada ka nemi waninsa, kada ka nemi yabo daga wajen mutane, kada ka jira wani sakamako sai a wajen Allah (S.W.T).

Ayyub Assakhatiyani ya kasance yana tsayuwar dare gabaxayansa, yana voye haka, idan safiya ta yi, sai xaga muryarsa kamar yanzu ya tashi.

Ikhlasi shi ne cikar aiki da kyansa, kuma shi ne mafi girman abu a duniya, shi ne kaxaita Allah da xa’a, da mantawa da cewa mutane suna ganinka, ta hanyar tunawa da cewa Allah yana ganinka, duk abin da aka yi don Allah to zai saka a kanshi, duk kuwa abin da aka yi don waninsa, to zai tafi a wofi. Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Dukkan ayyuka sai da niyya, kuma kowane mutum yana da sakamakon abin da ya yi niyya. Wanda hijirarsa ta kasance don duniya da zai samu, ko mace da zai aura, to sakamakon hijirarsa yana ga abin da ya yi hijira zuwa gare shi”. (Bukhari ne ya rawaito shi)

Matsayin Ikhlasi

Ikhlasi yana da matsayi babba a addini, wanda babu abin da ya kai shi matsayi, ba a karvar aiki sai da tsarkake niyya, Allah Maxaukakin Sarki ya tunatar da mu Ikhlasi a wurare da dama a cikin Alqurni mai girma, daga ciki akwai faxin Allah Maxaukakin Sarki “Ba a umarce su sai dai su bautawa Allah suna masu tsarkake addini gare shi” (Albayyinah : 5)

Kuma Allah mai girma da buwaya ya ce, “Ka ce haqiqa sallata da yankana da rayuwata da mutuwata na Allah ne Ubangijin talikai. Ba shi da abokin tarayya, da wannan aka umarce ni, nine farkon musulmi” (Al’an’am : 162 – 163)

Allah mai girma da buwaya ya ce, “Wanda ya halicci mutuwa da rayuwa don ya jarrabeku wanene a cikinku ya fi kyan aiki” (Al-mulk : 2)

Kuma Ya sake cewa : “Haqiqa mun saukar maka da littafi da gaskiya, ka bautawa Allah kana mai tsarkake masa addini, ku saurara addini. Tsarkakakken addini na Allah ne” (Azzumar : 2 – 3)

Kuma Ya ce, “Wanda yake fatan gamuwa da Ubangjinsa to ya yi aiki na qwarai kada ya haxa wani da Ubangijinsa a wajen bauta” (Alkahfi : 110)



Tags: