Allah Makusanci

Allah Makusanci

Allah Makusanci

Lallai Allah makusanci

Ya wanda yake kusa da wanda ya kira shi, ya wanda yake kusa da wanda ya yi fata nagari gare shi.

Ya wanda yake kusa da wanda ya roqe shi, ya wanda yake kusa da mu fiye da jijiyar wuyanmu

Ka yi mana baiwar samun xebe kewa da kai, da zancenka, ya wanda yake kusa .. “Idan Bayina suka tambayeka danagane da ni, ka ce ni a kusa nake” (Albaqra : 186)

“Makusanci”

Makusanci a cikin xaukakarsa da iliminsa da tsinkayensa na dukkan komai

Makusanci ga kowa da kowa da iliminsa, da saninsa, da kulawarsa, da ganin abin da ake, da kewayewarsa da sanin komai

“Makusanci”

Ga wanda ya kira shi, yana bayarwa yana tausayawa, yana xagewa ya yaye, ya amsawa wanda yake cikin buqata.

“Makusanci”

Ga wanda ya tuba zuwa gare shi, ya ta’allaqa da shi, yana gafarta zunubai, yana karvar tuba.

“Makusanci”

Yana karvar abin da bawansa ya kusance shi da shi, yana kusantar bawansa gwargwadon yadda bawan ya kusance shi.

“Makusanci”

Wanda yake ganin dukkan yanayin da bayinsa suke ciki, babu wani abin da yake voye masa

“Makusanci”

Makusanci da tausayinsa, da kiyayewarsa, da taimakonsa, da qarfafawarsa, wannan na musamman ga bayinsa waliyyansa kaxai.

“Makusanci”

Zuwa gare shi bayinsa za su koma a qarshen lamarinsu..“Mu muka fi kusa da shi fiye da ku” (Alwaqi’a : 85)

“Makusanci”

Zukata suna nutsuwa da shi, su na farin ciki da ambatonsa.

Lallai Allah Makusanci ne



Tags: