Allah ne mai ciyarwa

Allah ne mai ciyarwa

Allah ne mai ciyarwa

Haqiqa Shi Allah mai ciyarwar ne “Allah ya kasance mai kiyayewa akan dukkan komai” (Annisa’i : 85)

Mai ciyar da kowa da komai.. Wanda ya isar wa da dukkan komai abin da zai ci, ya ba wa dukkan halitta arziqinta, ya sarrafa shi yadda ya ga dama da hikimarsa da godiayrsa.

“Wanda yake ciyar da kowa”

Wanda ya isarwa da dukkan halittu abincinsu, ya halitta musu abin da za su rayu da shi, ya ba su abin da za su sha ya qosar da su, ya ba su rayuwa mai kyau.

Mai ciyarwa

Wanda yake ciyar da zukata da ilimi kala-kala, ta rayu da shi, hankula su kwanta da shi.

Ya Allah wanda yake tsaye da sha’anin bayi, da jujjuya rayuwarsu da makomarsu, kiyayewarka da afuwarka da lafiyarka muke nema.. “Allah ya kasance mai kiyayewa akan dukkan komai” (Annisa’i : 85)

Haqiqa Allah shi ne mai ciyar da dukkan komai mai kula da shi.



Tags: