Allah shi ne Mai tilastawa

Allah shi ne Mai tilastawa

Allah shi ne Mai tilastawa

Haqiqa Shi ne Allah mai girma da buwaya mai tilastawa. “Shi ne Allah wanda babu abin bautawa sai shi, mai mulki, tsakakakke, mai aminci, mai gaskatawa, mai kulawa, mabuwayi mai tilastawa, mai nuna isa, tsarki ya tabbata gare su daga barin abin da suke siffata shi da shi” (Al-hashru : 23)

“Mai Mikarwa”

Mai xora karyayye, mai taimakon fursuna, mai wadatar da talaka, mai tayar da masu tuntuve, mai gafarta zunuban masu zunubi, mai yanta waxanda suke cikin azaba, mai tayar da zukatar masoya masu tsoronsa.

“Al-jabbar”.. ma’ana maxaukaki, mai rinjaye, mai tausayi, mai miqar da karyayyun zukata, da gajiyayye mai rauni, da wanda ya fake a wajensa.

“Mai rinjaye”

Wanda xaukakarsa ta cika, ni’amarsa ta girmama a kan dukkan komai

“Mai qasaita”

Wanda komai da komai suka sunkuya masa, suka sallama masa, babu wani abu da yake shagaltar da shi daga wani abu.

“Mai qasaita”

Ma’abocin qasaita, da sarauta, da isasshen mulki, da girma da xaukaka

‘Mai rinjaye”

Wanda dukkan masu girman kai suka sunkuya masa, masu girma suka karaya a gabansa, masu mulki da manya suka qasqanta a gabansa, masu laifi da xagawa suka zube a gabansa.

Haqiqa Shi ne Allah Mai tilastawa ne



Tags: